1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An koma kai wa juna hare-hare a Sudan

June 22, 2023

A Sudan ana jin karar wasu manyan makaman artillery a brinin Khartoum, bayan yarjejeniyar tsagaita wuta ta kwanaki uku da aka cimma a kasar ya kawo karshe.

Hoto: REUTERS

Mazuana birnin Khartoum sun ce ana ta musayar wuta tsakanin dakarun gwamnati da bangaren mayakan da ke biyayya ga tsohon mataimakin shugaban kasa Mohammad Hamdan Daglo, a Khartoum din da kuma yankin Omdurman.

Haka ma akwai rahotannin wani fada a Dilling da ke a kudancin Kordofan, yankin mai tazarar wasu daruruwan kilomitoci da fadar gwamnatin kasar.

A farkon wannan makon ne dai aka tsagaita wutar domin ba da damar kai agajin jinkai a yankunan da ke matukar bukatar taimako.

Sama da mutum dubu biyu dai sun salwanta a Sudan, wasu sama da miliyan biyu da dubu 200 kuma sun tsere daga kasar tun bayan barkewar sabon yaki a ranar 15 ga watan Afrilu.