An koma kai wa juna hare-hare a Sudan
June 22, 2023
Talla
Mazuana birnin Khartoum sun ce ana ta musayar wuta tsakanin dakarun gwamnati da bangaren mayakan da ke biyayya ga tsohon mataimakin shugaban kasa Mohammad Hamdan Daglo, a Khartoum din da kuma yankin Omdurman.
Haka ma akwai rahotannin wani fada a Dilling da ke a kudancin Kordofan, yankin mai tazarar wasu daruruwan kilomitoci da fadar gwamnatin kasar.
A farkon wannan makon ne dai aka tsagaita wutar domin ba da damar kai agajin jinkai a yankunan da ke matukar bukatar taimako.
Sama da mutum dubu biyu dai sun salwanta a Sudan, wasu sama da miliyan biyu da dubu 200 kuma sun tsere daga kasar tun bayan barkewar sabon yaki a ranar 15 ga watan Afrilu.