1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sabuwar tattaunawa da sojojin Sudan

May 14, 2019

Bayan afka wa masu zanga zangar neman kafuwar mulkin farar hula da yayi sanadiyyar rayuka a Sudan, an bude sabon zagayen tattaunawa da majalisar mulkin sojin kasar.

Sudan, Khartoum: Situation nach dem Putsch im Sudan
Hoto: picture-alliance/dpa


A Talatar nan ce aka sake komawa kan teburin tattaunawa tsakanin jagororin mulkin Sojin kasar Sudan da na bangaren masu zanga-zangar, domin ganin an maida mulki hannun farar hula, biyo-bayan barkewar wani sabon rikici a daren jiya Litinin da ya yi sanadiyyar hallaka mutum shida ciki har da jami'in tsaro guda. 

Masu zanga-zangar dai sun taka gagarumar rawar da ta kawo karshen mulkin kama-karya na shekaru 30 na Al-Bashir, sai dai bayan sojoji sun hambarar da shi sai suka zama 'yan kama-wuri-zauna, lamarin da ya fusata matasan sake fantsama kan titunan kasar suna kiraye-kirayen mika mulkin hannun farar hula.

Amurka dai ta zargi rundunar Sojin kasar da hannu wajen harin na jiya da ya yi sanadiyyar mutuwar mutum shida.