1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An rusa gwamnati a Equitorial Guinea

Zainab A MohammedAugust 11, 2006

Rahotanni daga Equitorial Guinea na nuni dacewa shugaban kasar Teodoro Obiang Nguema Mbasogo,ya tilastawa prime minista da ministocinsa yin murabus daga mukamansu,wanda zai samar da daman yin garon bawul a gwamnatin wannan kasa dake zama ta 3 a jerin kasashen Afrika masu arzikin man petur.A jiya nedai Shugaba Obiang,wanda ke rike da mulkin Guinea tunda ta samu yancin kai a 1979,a hukuman ya amince da takardun murabus din premier Abia Biteo Borico,da sauran mukarraban gwamnatinsa a wannan kasa dake yammacin Afrika.Shugaba na Guinea dai yasha zargin gwamnatin kasar da rashin inganci musamman a bangaren kula da lafiya da inganta ilimi.Anasaran Shugaba Obiang zai sanar da sabon Prime minista cikin yan kwanaki masu gabatowa.