1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An yi garkuwa da Bajamushe limamin coci a Mali

Abdul-raheem Hassan
November 21, 2022

An gano motar Hans-Joachim Lohre a Bamako, babban birnin kasar Mali kusa da makarantar da yake koyarwa. Mutumin wanda asalin dan kasar Jamus ya kai shekaru 30 yana aiki a Mali.

Sojan Barkhane a Mali
Hoto: Philippe De Poulpiquet/MAXPPP/dpa/picture alliance

Wasu da ake zargin masu kaifin kishin addini sun yi garkuwa da wani limamin coci dan kasar Jamus a Bamako babban birnin kasar Mali, Wannan dai shi ne karon farko cikin shekaru 10 da aka sace wani dan kasar yammacin duniya a Mali.

Kawo yanzu dai babu wanda ya dauki alhakin yin garkuwa da limamin cocin, wanda ya shafe fiye da shekaru 30 a Mali, sai dai tuni aka dora zargi kan kungiyar IS mai tarihin garkuwa da 'yan kasashen waje don samun kudin fansa.

Tsallake zuwa bangare na gaba Babban labarin DW

Babban labarin DW

Tsallake zuwa bangare na gaba Karin labarai daga DW