An sace sama da mutane 150 a Najeriya
April 4, 2026
Jami'an tsaron Nigeriya na bin sawun ‘yan bindiga bayan da suka sace mazauna wasu ƙauyuka a yankin arewa maso yammacin jihar Zamfara, kamar yadda ‘yan sanda suka tabbatar, lamarin da ya kasance ɗaya daga cikin manyan hare-hare na baya-bayan nan a yankin.
‘Yan bindigan sun kai hari ƙauyukan Kurfa Danya da Kurfan Magaji da ke yankin Bukkuyum a ranar Alhamis, inda suka buɗe wuta kan motoci da gidaje kafin su sace mutane.
Harin ta'addanci a arewacin Najeriya ya halaka mutane 45
Shugaban ƙaramar hukumar, Umar Abubakar Faru, ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa sama da mutane 150, galibi mata da yara, aka sace tare da kaisu cikin dazuzzukan da ke kewaye da yankin.
Lamarin ya tilasta wa mazauna tserewa tare da barin ƙauyukan da abin ya faru kuma ba a san inda wasu suka shiga ba.
Hatsarin kwale-kwale ya hallaka gomman mutane a Zamfara
‘Yan sandan jihar Zamfara sun tabbatar da aukuwar harin, amma sun ce har yanzu ana ci gaba da tantance adadin mutanen da aka sace.