Koma baya a yaki da cutar Polio a Najeriya
September 5, 2016Talla
Hukumar Lafiya ta Duniya WHO ta tabbatar da cewa an gano bullar kwayar cutar Polio karo na uku a Najeriya. Ana danganta rashin nasarar kakkabe cutar daga Najeriya da rikicin Boko Haram, saboda yaro na uku da aka gano yana dauke da cutar yana cikin yankin da dakarun gwamnati suka kwato daga hannun mayakan kungiyar ta Boko Haram. Sannan biyu daga cikin masu dauke da cutar suna wani sansanin 'yan gudun hijira da ke karkashin kulawar sojojin Najeriya. Hukumar Lafiya ta Duniyar ta ce cutar ta Polio ta kwashe shekaru biyar tana yaduwa a jihar Borno da ke fama da rikici mai nasaba da tsagerun Boko Haram tun shekara ta 2009.