An soma ganin alamun sasanta Hamas da Isra'ila
October 8, 2025
Talla
Rahotanni daga kasar Masar na cewa akwai alamun samun ci gaba mai kyau a tattaunawar kai tsaye ta hannun masu shiga tsakanin Isra'ila da Hamas, kamar yadda shugaban kasar Masar Abdel Fattah el-Sisi ya bayyana.
A yau Laraba, jakadu daga Amurka sun shiga cikin tattaunawar da ke gudana a kan shirin samar da zaman lafiya da Amurka ta gabatar.
Haka kuma, Firaministan Qatar da shugaban hukumar leken asirin Turkiyya sun isa birnin Sharm el-Sheikh, inda ake ci gaba da tattaunawar tun a ranar Litinin.
Shugaban Turkiyya, Recep Tayyip Erdoğan, ya bayyana cewa shugaban Amurka Donald Trump ne ya roki gwamnatin Ankara da ta taimaka wajen shawo kan Hamas domin cimma yarjejeniya.