1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kungiyar AU ta kasashen Afirka na taronta karo na 37

Abdourahamane Hassane
February 15, 2024

A karshen mako ne ake soma gudanar da taron shugabannin kasashen kungiyar Tarayyar Afirka AU a Addis Abbaba babban birnin kasar Habasha karo na 37,

Nigeria | ECOWAS-Staatsoberhäupter in Abuja 2023 | Regionale Zusammenarbeit
Hoto: Kola Sulaimon/AFP

Tun farko a ranar Larabar majalisar zartaswar ta kungiyar da ta kunshi ministocin harkokin waje ta bude taron share fage. Sabbin juyin mulki da aka yi Nijar da Gabon da, rikicin siyasar Senegal, da Jamhuriyar Demokaradiyyar Kwango da sauran wasu batutuwan taron zai fi mayar da hankali a kansu  da kuma  shirin shigar kungiyar a cikin kungiyar G20 a cikin watan Satumbar da ke tafe.Kasashen Nijar da Gabon ba za su kasance ba a taronba, bayan kungiyar ta dakatar da su saboda juyin mulkin da aka yi a cikin kasashen biyu