1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An tsaurara tsaro a Indiya

April 10, 2019

Yayin da ake haramar zabe a Indiya, an soma daukar matakan ganin komai ya tafi ba tare da samun wata rigima ba. Akwai dai bangarorin kasar da ke fama da rigingimu.

Indien Konflikt um Zugang von Frauen zu Sabarimala-Tempel
Hoto: Getty Images/AFP

Hukumomi a kasar sun baza dubban jami'an sanda da sauran wasu masu kayan sarki a sassan jihohi 29 da wasu cibiyoyi biyu na tarayya, gabanin zaben 'yan majalisar dokoki.

A mazabu 91 ne za a fara zaben a tashin farko a ranar Alhamis, zaben kuma da za a yi a matakai bakwai daban-daban, a kuma kammala ranar 19 ga watan gobe na Mayu.

An dai tsananta matakan tsaro a yankunan Jammu da kuma jihar Kashmir, wadanda duk ke fama da fitintinu.

Akwai wasu rahotanni da ke cewa dakaru za su yi sintiri na musamman, a dukkanin wuraren da ke kan hadarin fuskantar barazana lokacin zaben.