1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rushewar ginin makaranta ya kashe mutane a Jos

Zainab Mohammed Abubakar
July 12, 2024

Jami'an agaji na ci gaba da gudanar da aikin ceto bayan rushewar ginin makarantar Saint Academy da ke Jos lokacin da yara ke rubuta jarrabawa.

Saint Academy JosHoto: NEMA Nigeria/X

Rahotanni daga Najeriya na cewa, gawarwaki da dama ne aka samu a karkashin baraguzan makarantar da ta ruguje a jihar Filato da ke tsakiyar kasar a wannan Juma'a.

Ginin mai hawa biyu, mallakar Saint Academy da ke unguwar Busa Buji  cikin gunduwar Jos ta arewa, ya rushe ne a lokacin makaranta da misalin karfe 07:30 agogon GMT, wanda ya sanya damuwa kan halin da dalibai da malamai ke ciki.

Ya zuwa yanzu dai an ceto dalibai biyar da ransu., a yayin da ake cigaba da aikin ceto  tare da jami'an tsaro ciki har da sojoji da 'yan sanda a wurin.