1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

'Yan bindiga sun sace mutane a Birnin Gwari

Binta Aliyu Zurmi
January 28, 2021

An sace mutane 30 a yankin Birnin Gwari da ke jihar Kaduna.

Symbolbild islamistischer Kämpfer
Hoto: Fotolia/Oleg Zabielin

A jihar Kadunan Najeriya 'yan bindiga sun yi awon gaba da wasu mutane 30 a yayin da suka kashe wani mutum guda a wani hari da suka kai a kauyen Kungi da ke yankin Birnin Gwari.

Da misalin karfe biyu na rana maharan suka isa kauyen a kan mashina suka shiga gida-gida suna zaban wadanda za su dauka, wani shaidan gani da ido ya ce yanzu haka kauyen na cikin zaman dar-dar.


Duk da cewar a kwai jami'an tsaro amma hakan bai hana maharan kaddamar da harin ba dama tafiya da mutanen ba tare da jami'an tsaro sun kai musu dauki ba a cewar wani mazaunin garin wanda yanzu haka aka tafi da mutum uku daga cikin 'yan uwansa.

 

Tsallake zuwa bangare na gaba Babban labarin DW

Babban labarin DW

Tsallake zuwa bangare na gaba Karin labarai daga DW