1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaTurai

Ana dab da cika shekaru hudu da yakin Ukraine

February 22, 2026

Rasha ta yi luguden bama-bamai da makamai masu linzami da ke cin dogon zango a birnin Kyiv na Ukraine, kwana biyu kafin cika shekara hudu da fara yaki.

Wani ginin Ukraine a birnin Lviv da Rasha ta kai wa hari
Wani ginin Ukraine a birnin Lviv da Rasha ta kai wa hari Hoto: Lviv Regional Military Administration/Anadolu Agency/IMAGO

Wani 'dan jaridar kamfanin dillancin labarai na AFP ya tabbatar da jin karar tashin bama-baman a birnin Kyiv. Kazalika, mai magana da yawun dakarun sojin Ukraine a birnin, Tymur Tkachenko, ya tabbatar da kai hare-haren, inda ya ce makiya sun kai musu farmaki, tare kuma da yin kira ga daukacin al'ummar birnin da su gaggauta neman mafaka a mabuyar da hukumomin kasar suka tanadar ta karkashin kasa.

Karin bayani:Ko za a yi sulhu tsakanin Rasha da Kiyv?

A ranar 24 ga watan Fabrairun 2026, za a cika shekaru hudu da fara yakin Rasha da Ukraine, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar dubban mutane daga kowanne bangare.

Karin bayani:Ukraine ta kai wa Rasha kazamin hari a masana'antar kera makamai

Shugaban kasar Ukraine Volodymyr Zelensky, na fuskantar matsin lamba daga Amurka wajen amincewa da sabon daftarin wanzar da zaman lafiya a yankin. Kazalika, ana sa ran gudanar da tattaunawa a kwanaki masu zuwa tsakanin Ukraine din da kasashen Turai da kuma wasu kasashen Gabas ta Tsakiya har ma da Turkiyya don lalubo bakin zaren kawo karshen yakin.