1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ana gudanar da zaben 'yan majalisar dokokin kasa a Iraki

November 11, 2025

Miliyoyin mutane a Iraki sun fita rumfunan zabe domin zaben wadanda za su wakilce su a majalisar dokokin kasar. Zaben na zuwa ne yayin da Iraki ne kokarin farfadowa daga matsalolin da yake-yake suka haddasa mata.

Wani allon tallar dan takara a zaben Iraki a birnin Bagadaza a jajibirin zabe
Wani allon tallar dan takara a zaben Iraki a birnin Bagadaza a jajibirin zabeHoto: Ahmad Al-Rubaye/AFP/Getty Images

‘Yan kasar Iraki na kada kuri’a domin zaben sabbin ‘yan majalisa, a zaben da Amurka da Iran; manyan kasashe masu tasiri a yankin ke sa ido sosai a kansa.

Zaben na ranar Talata na gudana ne a lokacin da Irakin ke fama da matsalolin cin hanci da lalacewar hanyoyi da tabarbarewar yanayi na ayyuka, duk da dan natsuwar da ta samu a ‘yan shekarun baya.

Fiye da masu zabe miliyan 21 ne suka yi rajista domin zabar ‘yan majalisa 329 daga cikin ‘yan takara sama da 7,700, yayin da kasar ke ci gaba da farfadowa daga tasirin yake-yake bayan kifar da gwamnatin marigayi Shugaba Saddam Hussein.