1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

MDD ta zargi China da cin zarafi a Xinjiang

Abdul-raheem Hassan
September 1, 2022

Ofishin kare hakkin bil adama na Majalisar Dinkin Duniya, ya zargi China da yuwar aikata laifi kan bil'adama bayan wani sabon rahoto ya nuna wariyar launin fata da China ta yi wa 'yan kabilar Uygur a jihar Xinjiang.

China, Xinjiang
Hoto: Michael Reynolds/dpapicture-alliance

Rahoton ya ce zargin nau'ikan azabtarwa ko musgunawa da munin yanayin wurinj tsare mutane, tabbaci ne na irin wulakancin da gwamnatin Bejin ke aiwatarwa kan musulmai tsirarru.

Kungiyar Amnesty International da Human Rights Watch da sauran kungiyoyi sun dade suna zargin China da tsare 'yan kabilar Uygur fiye da miliyan daya a yankin Xinjiang. Sabon rahoton na Majalisar Dinkin Duniya ya ce lamarin na bukatar kulawar gaggawa daga gwamnati, hukumomin Majalisar da tsarin kare hakkin bil adama, da ma sauran kasashen duniya baki daya.