Somaliya: Ana zargin tura sojoji Habasha
January 27, 2021![Somalia Tabda| Kenianische Soldaten | Militäroffensive](https://static.dw.com/image/55946351_800.webp)
Talla
Matakin da ya kai ga 'yan majalisar dokoki rubuta wasika ta musamman na neman karin bayani ga Shugaban kasar Somaliya a madadin iyayen da suka zaku su san halin da yayansu ke ciki.
Gwamnatin Somaliyar dai ta musanta zargin tura sojojin kasar shiga yaki a Tigray, tare da cewa gwamnatin Habasha ba ta taba neman agajin sojojin daga Somaliya ba.