AU ta yi Allah Wadai da harin Somaliya
February 29, 2016![Somalia Anschlag Explosion in Baidoa](https://static.dw.com/image/19081536_800.webp)
Talla
Birnin dai na Baidoa wanda ke samun kulawar dakarun hadaka na rundunar Tarayyar Afrika kimanin dubu 22 mai suna AMISOM ya fuskani harin kungiyar ta al-Shabbab ne a ranar lahadi nan. A inda mutane kimamin 30 suka hallaka a yayin da wasu 61 suka samu raunuka daban-daban.
A nasa bangaren gwamnan birnin Abdurashid Abdullahi ya ce, daga cikin wadanda suka sami raunuka, 15 suna nan cikin mawuyacin hali a inda ya kara da cewar harin ya faru akan cikin tsakiyar wani wajen hada-hadar harkoki ciki da mutane a birnin na Baidoa.
Tuni dai kungiyar ta Al-shabbab ta yi ikirarin cewar itace ke da alhakin harin na Somaliya.