1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

AU ta yi maraba da kwance wa 'yanbindiga damara a CAR

July 18, 2025

An shafe lokaci ana fama da fadace-fadacen 'yanbindiga a Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya sannan an kashe mutane da dama.

Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya na fama da yake-yake tun bayan 'yancin kai a 1960
Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya na fama da yake-yake tun bayan 'yancin kai a 1960Hoto: Solomon Muchie/DW

Kungiyar Tarayyar Afirka AU ta yi maraba da kwance wa wasu manyan kungiyoyin 'yanbindiga guda biyu damara a Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya.

A sanarwar da ta fitar ranar Juma'a, AU ta kuma yi kira ga sauran masu dauke da makamai da su ajiye makamansu.

Halin kunci a Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya

Jamhuriyar CAR na daga cikin kasashe mafiya talauci a duniya, kuma ta sha fama da jerin yake-yaken basasa da kuma mulkin kama-karya tun bayan samun 'yancin kai a shekarar 1960.

Duk da yarjejeniyar zaman lafiya da aka cimma a 2019 tsakanin gwamnatin kasar da kungiyoyi 'yantawaye guda 14, har yanzu wasu kungiyoyi dauke da makamai na ci gaba da fada da ikirarin iko da wasu sassan kasar.

MDD ta ce yakin Sudan zai iya shiga Afirka ta Tsakiya

A cikin wata sanarwa da aka wallafa a kafafen sada zumunta, Shugaban AU, Mahmoud Ali Youssouf, ya yi maraba da matakin ajiye makamai da kungiyoyin da suka hada da UPC da 3R, suka yi kamar yadda shugabanninsu suka sanar a ranar 10 ga watan Yulin 2025.