SiyasaAfirka
Shugaban rundunar ‘yan sandan Kenya ya yi murabus
July 12, 2024
Talla
Shugaban rundunar ‘yan sandan Kenya ya yi murabus daga mukaminsa, sakamakon sukar da aka yi masa kan zanga-zangar kin jinin gwamnati da ta yi sanadin mutuwar mutane da dama, a cewar fadar shugaban kasa, wanda shi ne babban jami'i na baya bayan nan da guguwar zanga-zangar ta yi awon gaba da shi.
Shugaba William Ruto ya amince da murabus din Japhet Koome, babban sufeton 'yan sandan kasar, a cewar wata sanarwa da fadar shugaban kasar ta fitar.