1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Badakalar siyasar kasar Masar

February 6, 2014

Shugaban rundunar sojojin kasar Masar da ya jagoranci kifar da zababbiyar gwamnatin Dimokaradiyar kasar, ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar shugaban kasa.

Hoto: Reuters

Wannan aniya ta Field Mashal Abdel Fattah al-Sisi, da aka dade ana jiran bayyanar ta a fili dai, ka iya kara rura wutar tashe-tashen hankulan da Masar din ke fama da su tun bayan da Al-Sisin ya jagoranci sojoji suka kifar da gwamnatin hambararren tsohon shugaban kasar Muhammed Morsi a shekarar da ta gabata.

Wata jaridar kasar Kuwaiti ta ruwaito Al-Sisi na cewa ba zai ki amincewa da kiraye-kirayen tsayawa takara da al'ummar kasar Masar din ke yi masa ba, a dangane da hakan zai tsaya takarar shugabancin kasar a zabukan da za a gudanar a nan gaba. Masana dai na bayyana wanannan aniya ta Al-Sisi da cewa Masar din za ta sake komawa kan tafarkiun mulkin soja bayan gagarumin juyin-juya halin da ya afku a kasar a shekara ta 2011 da ya yi awon gaba da kujerar mulkin tsohon shugaban kasar Hosni Mubarak.

Mawallafiya: Lateefa Mustapha Ja'afar
Edita: Umaru Aliyu