Baki 'yan kasashen waje sun halaka a wani hari a Tunisiya
June 26, 2015Talla
Mutane sama da ashirin ne suka rasu bayan da wani dan bindiga dadi ya kai hari a wani otel a garin Sousse da ke samun baki daga kasashen waje a Tunisiya. Mai magana da yawun ma'aktar harkokin cikin gidan kasar ta Tunisiya ya bayyana haka a ranar Juma'an nan.
A cewar Mohamed Ali Aroui da ke magana da yawun ma'aikatar harkokin cikin gidan Tunisiya ya ce wannan hari dai an kai shi ne a wani otel da ake kira Marhaba da 'yan yawon bude ido ke sauka a cikinsa idan sun isa kasar ta Tunisiya.
A kwai mutane daga kasashen waje da ke wasanni a farfajiyar otel din hada da yin linkaya a cikin ruwa da aka tanada ga masu sha'awa. Har yanzu dai ba a bayyana kasashen da mamatan su ka fito ba.