Ban da Brahimi sun yi wa bangarorin da ke cikin rikicin Siriya tayin shiga tsakaninsu
March 3, 2013![](https://static.dw.com/image/16193140_800.webp)
Talla
Bayan wani zama da suka yi kusa da yankin Lusanne na kaasr Switzerland, babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya(MDD) Ban Ki Moon, da manzon kasa da kasa na musamman a Siriya, Lakhdar Ibrahimi sun ce Majalisar Dinkin Duniya za ta yi madallah da duk wata tattanawar da za a shirya tsakanin wani wakili mai karfi daga bangaren 'yan adawa da kuma wata karfaffar tawwaga ta gwamnatin Siriya. Ita dai MDD ta kuduri niyyar taimaka ma wannan tattaunawar. A cikin jawabinsu na hadin-gwiwa bayan ganawar tasu Ban da Brahimi sun ce sun tattauna akan kalaman da aka jyo a baya-bayan nan daga bakin 'yan adawa da kuma gwamnati da ke bayyana niyarsu ta shiga tattaunawa.
Mawallafiya: Halima Balaraba Abbas
Edita: Umaru Aliyu