1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Barazanar kungiyar IS a kasar Libiya

Salissou BoukariFebruary 2, 2016

A yayin da ake kokarin kafa gwamnatin hadin kan 'yan kasa a Libiya, kungiyar IS reshen Libiya na kasancewa barazana ganin yadda take kaiwa ga arzikin man fetir.

Libyen Kämpfe gegen IS in Sirke
Hoto: picture-alliance/Photoshot/Hamza Turkia

Masu ikirarin jihadin na IS a Libiya dai da ke rike da birnin Syrte, na amfani ne da yanayin da kasar ke fuskanta na rashin tsayayyar gwamnati inda sau tari suka kai hare-hare ga ma'aikatun man kasar. Da yake magana kan wannan batu na kasar Libiya, sakataren harkokin wajen Amirka John Kerry da ke halartar wani zaman taro a birnin Roma na kasar Italiya, ya ce a daidai lokacin da ake daf da samun gwamnatin hadin kan 'yan kasa, bai kyautu ba a ce 'yan jihadin kasar ta Libiya sun kai ga samun biliyoyin dalar Amirka daga man da suke sata ba.

Tsallake zuwa bangare na gaba Babban labarin DW

Babban labarin DW

Tsallake zuwa bangare na gaba Karin labarai daga DW