1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaTurai

Barcelona ta rattaba hannu da DRC kan tallata yawon bude

July 17, 2025

Jamhuriyar Demokradiyyar Kwango ta amince da biyan sama da Yuro miliyan 40 a wata yarjejeniya da kungiyar kwallon kafa ta Barcelona.

Yan wasan Barcelona Lamine Yamal da Raphael Dias Belloli (Raphinha) da kuma Robert Lewandowski
Yan wasan Barcelona Lamine Yamal da Raphael Dias Belloli (Raphinha) da kuma Robert Lewandowski Hoto: Alberto Gardin/NurPhoto/picture alliance

Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya samu ganin daftarin yarjejeniyar da aka cimma tsakanin Kinshasa da Barcelona, wanda Kwango za ta rinka biyan kungiyar Yuro miliyan 11.5 a duk shekara har tsawon shekaru hudu, domin bunkasa fannin yawon bude ido na kasar a rigunan 'yan wasan kungiyar.

Karin bayani:Ruwanda: Ko karshen rikici da Kwango yazo?

Ministan Wasanni na DRC Didier Budimbu ya shaida wa  Reuters cewa baya ga Barcelona, kungiyoyin kwallon kafar irin su AC Milan da AS Monaco sun bukaci kulla yarjejeniya na kimanin Yuro miliyan 1.6 a duk kakar wasanni da AS Monaco da kuma na Yuro miliyan 14 a duk kakar wasanni da AC Milan.

Karin bayani:Barcelona ta isa Paris don cinikin Neymar

A watan Fabrairun 2025, ministar harkokin wajen Kwango Therese Kayikwamba Wagner ta bukaci kungiyoyin kwallon kafar Arsenal da Bayern Munich da kuma Paris St Germain  da su kawo karshen tallata Ruwanda a rigunan 'yan wasansu, sakamakon rawar da take takawa da rikicin DRC da M23.