1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Bincike kan harin iyakar Turkiyya da Siriya

May 14, 2013

Mahukuntan Siriya sun ce a shirya su ke da su shiga a dama da su wajen bincike na hadin gwiwa game da harin nan da aka kai garin Reyhanli da ke kan iyakar kasashen biyu.

epa03695968 People help victims after an explosion in Reyhanli District, Hatay, Turkey 11 May 2013. At least 13 people were killed and 22 wounded following explosions on 11 May in southern Turkey near the Syrian border, Turkish television NTV reported. Initial reports said two car bombs exploded in Reyhanli, a town in the province of Hatay, which borders Syria. EPA/CEM GENCO/ANADOLU AGENCY TURKEY OUT EDITORIAL USE ONLY/NO SALES/NO ARCHIVES EDITORIAL USE ONLY/NO SALES/NO ARCHIVES EDITORIAL USE ONLY/NO SALES/NO ARCHIVES
Tote und Verletzte bei Anschlag in TürkeiHoto: picture-alliance/dpa

Ministan yada labaran Siriya Omran al-Zohbi ne ya shaidawa manema labari hakan a wannan Talatar inda ya ce gwamnatin Assad shirye ta ke da ta ga an gudanar da bincike kan harin domin tantance hakikanin wanda su ka kai shi.

A ranar Lahadin da ta gabata ce dai wasu 'yan kunar bakin wake su ka kai harin na garin na Reyhanli wanda ya yi sanadiyyar rasuwar mutane da dama, harin da hukumomin Turkiyya su ka ce wasu mutane da ke alaka da hukumar leken asirin Siriya ne su ka kai shi bayan da su ka ce sun kama mutane tara da su ke zargi da kai harin, zargin da Siriya ta musanta.

Mawallafi: Ahmed Salisu
Edita: Saleh Umar Saleh