Hari kan gangamin shugaban kasa a Habasha
June 25, 2018Talla
An dai kai wannan harin ne yayin wani gangami na neman hadin kan al'ummar kasar Habasha wajen sauye-sauyen da Firaministan Abiy Ahmed ke yi a karshen mako. Kafar yada labaran gwamnatin Habashan ta EBC ta ruwaito cewa tuni jami'an suka isa Habashan, inda suke taimakawa wajen gudanar da binciken. Sama da mutane 150 ne suka jikkata yayin harin, inda kawo yanzu mutane biyu suka rasa rayukansu sakamakon raunukan da suka samu yayin harin. Wani shaidar gani da ido ya bayyana cewa yaga wani mutum sanye da kayan sarki na jami'an tsaro na kokarin harba gurneti, a gangami da aka gudanar mafi girma da kasar da ke zaman ta biyu mafi yawan al'umma a Afirka.