Blinken ya shawarci Haiti ta kafa gwamnatin rikon kwarya
March 8, 2024![Haiti verlängert Ausnahmezustand](https://static.dw.com/image/68470397_800.webp)
A yayin tattaunawarsa da Firaministan Haiti, Antony Blinken ya bukaci Ariel Henry da ya gaggauta kafa gwamnatin mulkin rikon kwarya a matsayin mafita ga dambarwar da kasar ta fada tsawon shekaru uku.
Karin bayani: Fargabar dagulewar al'amura a Haiti
Babban jami'in diflomasiyyar na Amurka ya bukaci da a kafa gwamnatin rikon kwarya ta hadin kan kasar wace za ta kunshi dukannin bangarorin siyasa sannan kuma a shirya zabe cikin hanzari don dawo da Haiti kan tafarkin dimokuradiyya.
Tun bayan zaben shekarar 2016 har yanzu ba a sake gudanar da wani zabe a Haiti ba, hasali ma a halin da ake ciki kasar da ke tsibirin 'Caraïbe' ba ta da shugaban kasa da majalisar dokoki tun bayan kisan tsohon shugabanta Jovenel Moïse a shekarar 2021 watanni kalilan bayan nadin Ariel Henry da ke jagorantar kasar a yanzu a mukamin firaiminista.