An kai wa 'yan gudun hijira hari a Kamaru
August 2, 2020![Kamerun l Interventionsbrigade "Brigade d'intervention rapide"](https://static.dw.com/image/52280151_800.webp)
Talla
Yan ta'addar dai sun jefa gurneti ne a cikin wani dandazon 'yan gudun hijira a harin da suka kaddamar a safiyar Lahadin nan kamar yadda Medjeweh Boukar wani shugaban al'umma a yankin ya tabbatar.
Rikicin Boko Haram da ya addabi yankin tafkin Chadi bai bar Kamaru ba domin a watan Yuni na 2019 mayakan Boko Haram su wurin 300 sun kashe mutane 24 cikinsu har da sojojin Kamaru 16 da ke kan aiki a wani barikin sojoji.