Bulgariya na tattaunawa akan kafa asusun taimakon yaran Libya
January 21, 2006Talla
Bulgariya na ci-gaba da tattaunawa da Libya akan kafa wani asusun taimakawa iyalan kananan yara da suka kamu da kwayoyin HIV a Libya. To sai dai har yanzu ba´a bayyana yawan kudin da za´a zuba cikin wannan asusu ba. Ana sa rai wannan asudu zai taimaka a rage kace-nace da ake yi dangane da ma´aikatan jiya su biyar na Bulgariya da kuma wani likita Bafalasdine da aka same su da laifin yiwa yaran allurar kwaoyin cutar HIV a Libya. Iyayen yaran dai na son a ba su diyya da ta kai Euro miliyan dubu 4.3, to amma Bulgariya ta ki hakan tana mai cewa ma´aikatan jiyyan ba su da laifin kamuwa da HIV da yaran suka yi. A na sa ran sake yin shari´ar mutanen 6 nan da wata daya.