1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
Lafiya

Equatorial Guinea na fama da Marburg

Lateefa Mustapha Ja'afar
February 14, 2023

Bayan da Equatorial Guinea ta tabbatar da sake barkewar annobar kwayar cutar Marburg da ke kaman-cece-niya da Ebola, Hukumar Lafiya ta Duniya WHO ta tsaurara bincikenta kan cututtuka masu yaduwa a kasar.

Tedros Adhanom Ghebreyesus | Darakta Janar | Hukumar Lafiya ta Duniya WHO
Darakta Janar na Hukumar Lafiya ta Duniya WHO Tedros Adhanom GhebreyesusHoto: Andreas Arnold/dpa/picture alliance

Wakilin hukumar a Equatorial Guinea George Ameh ne ya tabbatar da matakin na WHO, inda ya ce suna bincike domin gano mutanen da suka yi hula da wadanda suka kamu da cutar ta hanyar dawo da ma'aikatan da suka gudanar da bincike kan kwayar cutar COVID-19 domin su taimaka. Tuni dai 'yar karamar kasar da ke yankin tsakiyar Afirka, ta sanar da mutuwar mutane tara daga kwayar cutar da kuma wasu 16 da ake kyautata zaton sun kamu da ita. Equatorial Guinea ta kumamma killace mutane sama da 200, tare da takaita zirga-zirga a gundumar Kie-Ntem da cutar ta fara bulla.