1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Farkamin soja ya kashe 'yan ta'adda 30 Burkina

Abdoulaye Mamane Amadou
February 24, 2019

Sojoji sun hallaka 'yan ta'adda akalla 30 a wani samamen da soja suka kai a mabuyar mayakan jihadi a sansanoni daban da ke gabashin kasar Burkina Faso

Burkina Faso Symbolbild Siccherheit
Hoto: Getty Images/AFP/I. Sanogo

 

Rahotanni sun ce rundunonin sojan kundunbala, hadin gwiwa da na sojan sama ne suka kai kai samamen a yankunan da ke a matsayin maboyar mayakan na jihadi.

Tuni ma'aikatar tsaron kasar Burkina Faso ta bayyana cewa, ko baya ga hallaka mayakan jihadin, rundunar sojan kasar ta yi nasarar kwato makamai da dama tare lalata tarin abinci.

Shekaru hudu kenan da  Burkina Faso ke fama ne da matsalolin tsaro musamman ma hare-haren ta'addanci wanda ya yi sanadiyar mutuwar mutane da dama ciki har da jami'an tsaron kasar.