Sojojin Burkina Faso sun kashe 'yan ta'adda 47
May 20, 2020![Afrika 2017 | Burkina Faso | Soldaten im Einsatz](https://static.dw.com/image/52105896_800.webp)
Talla
Shugaban askarawa na Burkina Faso Janar Moise Moningou ya ce harin na bazatan da suka kai a lardin Kossi da ke kan iyaka da Mali ya ba su damar lalata makaman 'yan ta'addar tare da kwace wasu. Tun daga shekara ta 2015 hare-haren 'yan ta'addar a Burkina Faso sun yi sanadiyyar mutuwar mutane 850 yayin da suka tilasta wa wasu kusan dubu 840 yin kaura.