1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An kashe mahaka zinare a Burkina Faso

Gazali Abdou Tasawa
October 6, 2019

A Burkina Faso mutane kimanin 20 sun halaka yayin harin da wasu 'yan bindiga suka kai a wata mahakar zinare ta gargajiya a kauyen Dolmane da ke arewacin kasar.

Kamfanin dillancin labaran Faransa na AFP ya ruwaito wasu majiyoyin tsaro na kasar ta Burkina Faso na cewa maharan dauke da bindigogi sun kai harin ne a yamamcin ranar Juma'ar da ta gabata, inda suka bude wuta kan mahaka zinaren tare da halaka 20 kana wasau da dama suka jikkata.

 A wannan yanki ne dama a tsakiyar watan Satumban da ya gabata, mayakan kungiyoyin da ke da'awar jihadi suka tarwatsa wata gada da ke kan hanyar biranen Djibo da Dori na arewacin kasar. A ranar Litinin din makon da ya gabata ma dai fararen hula tara ne suka halaka a cikin wasu jerin hare-hare da aka kai a garuruwan Pissele da Boulkiba na karamar hukumar Bourzanga ta jihar Bam a arewacin kasar, kana wasu mutane sama da 20 suka mutu a wasu jerin hare-haren a jihar ta Bam, lamarin da ya tilasta wa mutane sama da dubu 20 tserewa zuwa birnin Kongoussi.