1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rashin tsaro na kara yawa a Burkina Faso

Lateefa Mustapha Ja'afar
February 17, 2020

Rahotanni daga Burikina Faso na nuni da cewa wasu 'yan bindiga sun halaka mutane 24 tare da raunata wasu 18 suka kuma yi awon gaba da wasu mutane uku yayin wani hari da suka kai.

Burkina Faso | Anschlaf auf Hotel: Soldat vor dem Splendid Hotel in Ouagadougou
Hare-haren ta'addanci na kara yawa a Burkina FasoHoto: picture-alliance/AP Photo/S. Alamba

'Yan bindigar dai sun kai harin ne a wani Cocin Protestant da ke wani kauye a yankin Arewacin kasar. Haka kuma wata majiyar tsaro ta tabbatar da cewa sojojin kasar biyar sun halaka sakamakon bam da aka dana a kan hanya, a yankin da ke fama da tashe-tashen hankula. Gwamnan Lardin Kanal Salfo Kabore ya shaidawa kamfanin dillancin labaran Faranasa na AF cewa, gungun 'yan bindigar dauke da makamai sun kai harin ne a kauyen Pansi da ke Lardin Yagha inda suka halaka mazauna yankin bayan sun ware baki daga cikinsu.  Tun dai daga shekara ta 2015 kawo yanzu, mutane 750 ne aka tabbatar sun halaka yayin da wasua kimanin dubu 600 suka tsere daga gidajensu a Burkina Fason, da ke zaman guda daga cikin kasashe mafiya talauci a duniya da ke kuma fama da matsalar 'yan ta'adda masu tayar da zaune tsaye a yankin Sahel.