1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Yan bindiga sun kashe mutum 10

Ramatu Garba Baba
November 2, 2021

Yan bindiga sun kai hari tare da halaka fararen hula 10 a arewacin kasar Burkina Faso, kwana guda bayan kisan 'yan sanda biyar a yayin wani artabu da masu tayar da kayar baya.

Burkina Faso | Anschlaf auf Hotel: Soldat vor dem Splendid Hotel in Ouagadougou
Hoto: picture-alliance/AP Photo/S. Alamba

A yayin da al'umma a Burkina Faso ke tsakiyar jimamin kisan wasu jami'an 'yan sanda da 'yan bindiga suka halaka a karshen mako, wasu mahara sun sake kai wani sabon hari da yayi sanadiyar rayukan fararen hula goma. Yan bindigan sun afkawa mutanen ne, a yayin da suke kan hanyarsu ta zuwa cin kasuwan yankin da ke a arewacin kasar.

Hare-haren na ranakun Lahadi da Litinin, na zuwa ne a daidai lokacin da kasar ke bikin cika shekaru sittin da daya da kafa rundunar sojin kasar. Shugaba Roch Kabore a yayin jawabinsa ga manema labarai, ya ce, kasar ba za ta yi kasa a gwiwa ba duk da wadannan kalubale, a maimakon hakan ma, za ta kara zage damtse a yakin da take yi da ta'addanci.