1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Burkina Faso ta yanke wa wasu mutane 13 hukuncin kisa

August 12, 2025

Kotun Burkina Faso ta yanke hukuncin daurin rai-da-rai ga wasu mutane 13 sakamakon samunsu da laifin ayyukan ta'addanci, ciki har da wadanda suka kai hari ofishin jakadancin Faransa a 2018.

Shugaban gwamnatin sojin Burkina Faso Ibrahim Traore
Shugaban gwamnatin sojin Burkina Faso Ibrahim TraoreHoto: Donat Sorokin/TASS/dpa/picture alliance

Kotun ta Burkina Faso ta kuma yanke hukuncin daurin shekaru 10 zuwa 21 ga wasu mutanen akalla 60, wadanda ke da hannu a tada zaune tsaye da kuma kai harin ta'addanci hedikwatar sojojin birnin Ouagadougou da kuma ofishin jakadancin Faransa ta hanyar amfani da bindigogi da kuma tada bam a cikin mota.

Karin bayani: Gwamnatin Burkina Faso ta rufe fitaccen gidan rediyon kasar

Tashe-tashen hankula a kasar Burkina Faso ya halaka mutane sama da dubu 26,000 tun daga shekara ta 2015, ciki har da sojoji da fararen hula.

Karin bayani: An yi zanga-zangar goyon bayan sojojin da ke mulkin Burkina Faso

Rahoton kungiyar da ke tattara kididddigar mutanen da suka mutu a kasar ta ACLED ta ce rabin wadanda suka mutu sun rasa rayukansu ne a lokacin gwamnati mai ci ta Kyaftin Ibrahim Traore duk da yunkurin da yake yi na tabbatar da tsaro.