1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Burtaniya ta amince da Falasdinu a matsayin kasa

September 21, 2025

Burtaniya ta amince da kasar Falasdinu a hukumance, matakin ya sha bamban da tsohuwar matsayarta kan rikicin Isra'ila da Hamas. Kasashen Ostireliya da Kanada su ma sun bi sahu inda suka ayyana Falasdinu a matsayin kasa.

Firaministan Burtaniya Keir Starmer
Firaministan Burtaniya Keir StarmerHoto: Toby Melville/AFP/Getty Images

Firaministan Burtaniya, Keir Starmer, ya sanar da cewa daga wannan Lahadi,  a hukumance kasarsa ta amince da kasar Falasdinu. Wannan mataki ya saba wa tsohuwar matsayar Burtaniya, wadda ke cewa dole a jira a ga yadda tattaunawar tsagaita wuta ta kaya a tsakanin Isra'ila da kungiyar Hamas kafin amince da Falasdinun a matsayin kasa.

A watan Yuli, Mr. Starmer ya gargadi Isra'ila cewa Burtaniya za ta goyi bayan Falasdinu a Majalisar Dinkin Duniya idan Isra'ilan ba ta dauki matakin dakatar da rikicin Gaza ba. Wannan mataki ya sanya Burtaniya cikin jerin kasashe fiye da 140 da suka amince da Falasdinu.

Za a samu kasashe biyu a yankunan Falasdinu da Isra'ila?

02:08

This browser does not support the video element.

Kasashen Ostireliya da Kanada su ma sun amince da Falasdinun a matsayin kasa, inda firaminista Anthony Albanese na Ostireliya, da na Kanada, Mark Carney, suka ce hakan wani yunkuri ne na hadin gwiwa don farfado da mafita ta samar da kasashe biyu.

Karin bayani: Canada za ta goyi bayan kafa kasar Falasdinu

Firaministan  Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce zai ci gaba da adawa da wannan mataki, yana mai cewa kafa kasar Falasdinu zai kawo barazana ga Isra'ila.