Doka da odaRuwanda
Burtaniya ta yi nasara kan Rwanda a Kotu
June 1, 2026
Talla
Kasar ta Rwanda ta sanya hannu kan wata yarjejeniya da tsohuwar gwamnatin Burtaniya wadda Firaminista na yanzu Keir Starmer ya soke bayan da ya hau karagar mulki a 2024.
A karkashin yarjejeniyar da kasashen biyu suka sanya wa hannu, yan gudun hijira da suka shiga Burtaniya ta barauniyar hanya za a tasa keyarsu zuwa Rwanda inda daga nan za su rubuta takardar neman mafaka ko zama na dundundun a hukumance.
Sai dai gwamnatin da ta zo daga baya ta baiyana tsarin a matsayin wani choge kuma barnar dukiyar al'umma inda Firaministan Starmer yace Burtaniya ta biya biliyoyin kudade masu yawa a shirin da ba a zato zai wakana.