1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

CDC ta bukaci a fara sayen riga-kafin Afirka

Binta Aliyu Zurmi
May 5, 2022

Cibiyar da ke yaki da cututtuka masu yaduwa a nahiyar Afirka CDC, ta yi kira ga kasashen nahiyar da ke sayen alluran rigakafin corona daga kasashen Turai da su koma sayen wadan da aka samar a kasar Afirka ta Kudu.

John Nkengasong | Director of the Africa Centers for Disease Control and Prevention
Hoto: Mulugeta Ayene/AP/picture alliance

Cibiyar ta CDC dai ta yi wannan kiran ne a wani mataki na tallafawa kamfanin Aspen don ci gaba da samar da alluran a nahiyar a cikin sauki da ma rahusa.

A kokarin da cibiyar ke yi na ganin kamfanin da ke samar da alluran bai kai ga durkushewa ba a sabili da rashin masu sayen rigakafin. 

Mataimakin darakatan kamfanin ya ce duk masu sayen alluran daga kasashen Turai ya kamata su karkata akalarsu ga wadanda aka samar a gida.

Wannan dai shi ne kamfanin farko da ya fara samar da rigakafin corona a nahiyar Afirka, amma rashin samun masu sayen alluran rigakafin da suka samar na barazana ga durkushewar kamfanin.