1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Cece-kucen saya wa masarautar Kano motoci

Nasir Salisu Zango
May 6, 2025

A jihar Kano da ke arewacin Najeriya, ana ci gaba da kace nace dangane da wata takarda da ta fito da ke nuna an ware sama da Naira miliyan 600 don sayen motoci ga masarautar Kanon

Mota kirar Rolls-Royce
Mota kirar Rolls-Royce Hoto: AP

Gwamnatin Kano dai ta ce ta dauki wannan mataki ne bisa bin dukkan ka'ídojin kashe kudade da kyautata muradan al'umma don haka 'yan adawa ne kawai ke sukar lamirin matakin

Tun bayan bullar wata takarda mai dauke da tambarin ma' áikatar kananan hukumomi ta jihar Kano wacce ke kunshe da bayanan kashe wadannan kudade don gyara da sayen sabbin motoci ga masarautar Kano, mutane suka ajiye komai suka bude shafin tattaunawa kan wannan batu. Kwamarade Adnan Muktar Tudun wada matashi ne dan gwagwarmaya da ke ganin cewar an saba lamba domin bai kyautu a ware wadannan makudan kudaden don sayen motocin masarauta ba.

Sarkin Kano Muhammadu Sanusi IIHoto: Abdoulaye Mamane/DW

Sai dai kuma a ta bakin mashawarcin gwamnan Kano kan harkokin masarauta kuma masanin tarihin masarautar Kano Farfesa Tijjani Muhammad Naniya yana ganin cewar sukar raáyi ne kawai ya sanya yan adawa kuka kan wannan mataki domin tsohuwar magana ce da kowacce gwamnati ke bi, kasancewar tun tale tale an kwace ikon karbar haraji daga hannun sarakuna don haka ne ma ya zama wajibi gwamnati ce za ta ringa kashe musu kudi wajen tafiyar da harkokin su la'akari da cewar dukkan gwamnatocin baya babu wanda bai yi wa masarautar hidima ba.

Fadar masarautar KanoHoto: DW/A. Kabir

Malam Ibrahim Ado Kurawa masanin tarihin masarautar Kano ne ya ce wannan mataki ba yau ne farau ba kuma dole ne a yi amfani da kudin gwamnati a biya bukatun masarauta sai dai idan daina sarautar za a yi kacokan

Tuni dai wannan magana ta zama wani babban maudu'í da ke daukar hankali a shafukan sada zumunta musamman a wannan lokaci da ake zaman doya da manja tsakanin magoya bayan sarakuna biyu da ke zuba mulki a Kano.