SiyasaAfirka
Chad za ta aike da dakaru 750 zuwa Haiti don taimakawa tsaro
March 24, 2026
Talla
Kasar Chad za ta aike da dakaru 750 na jami'an tsaronta zuwa Haiti, domin tallafawa rundunar wanzar da zaman lafiya ta Majalisar Dinkin Duniya a kasar, kamar yadda ma'aikatar harkokin wajenta ta sanar yau Talata.
A bara ne Majalisar Dinkin Duniya ta yi wa rundunar kwaskwarima tare da karfafa ta, sakamakon tashin hankalin da kasar ta fuskanta na hare-haren 'yan daba da ke rike da wasu sassan kasar.
Karin bayani: Kara tura 'yan sandan Kenya zuwa Haiti
Alkaluman da Majalisar Dinkin Duniya ta fitar yau Talata, sun nuna cewa rikicin ya yi sanadiyyar mutuwar mutane sama da 5,500, daga watan Maris na bara zuwa Janairun bana.