1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Chadi: Sojoji sun halaka madugun adawa Yaya Dillo

February 29, 2024

Hukumomin Chadi sun sanar da mutuwar dan adawa Yaya Dillo Djérou a harin da sojojin kasar suka kai wa hedikwatar jam'iyyarsa, watanni biyu gabanin gudanar da zaben shugaban kasa.

Sojoji Chadi sun halaka madugun adawa Yaya Dillo
Sojoji Chadi sun halaka madugun adawa Yaya DilloHoto: Issouf Sanogo/AFP/Getty Images

Dama dai ana bayyana Yaya Dillo Djérou a matsayin babban abokin hamayyar shugaban gwamnatin mulkin sojan Chadi Janar Mahamat Idriss Déby Itno wanda ya dare kan karagar mulki bayan mutuwar mahaifinsa.

 A lokacin da yabayyana a gidan rediyo don yin cikakken bayani kan yanayin harin, ministan sadarwa Abderaman Koulamallah ya ba da rahoton mutuwar 'yan sanda hudu da mutuwar mutane uku a cikin 'yan jam'iyyar PSF.

Sanarwar mutuwar Mista Dillo ta zo ne kwana daya bayan tashe-tashen hankula a tsakiyar birnin N'Djamena, inda jami'an tsaro suka yi amfani da bindigogi tare da harba barkonon tsohuwa a kusa da hedkwatar jam'iyyar ta PSF, inda ya fake.

Karin bayani: Hari a Chadi ya hallaka mutane da dama

Gwamnati Ndjamena na zargin Yaya Dillo da kai hari a daren Laraba zuwa Alhamis a hedkwatar hukumar leken asiri ta ANSE, a matsayin ramuwar gayya kan kama dan jam'iyyarsa da aka yi. Wannan harin da Mista Dillo ya kai a cewar gwamnati ya yi sanadiyar mutuwar mutane da dama.