1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Rundunar sojin Chadi na neman ma'aikata

September 25, 2021

Gwamnatin wucin gadi ta kasar Chadi ta sanar da kudurinta na rubanya sojojin kasar daga 35,000 zuwa 60,000. Hukumomin na Chadi sun ce suna da burin cimma wannan murtadi daga nan zuwa karshen shekarar 2022.

Tschad Mahamat Idriss Déby
Hoto: Kenzo Tribouillard/AFP

A yayin da yake magana a gaban Majalisar Dokoki a ranar Jumma'a, Ministan Tsaron Kasar Daoud Yaya Brahim ya ce rundunar sojin Chadi tuni ta fara yunkurin daukar matasan kasar aiki, inda ta fara da daukar sabbin kananan sojoji. 


Brahim ya ce manufar hakan ita ce karfafa rundunar sojin Chadi yadda za ta iya tunkarar kalubalen tsaron da kasar ke fuskanta da bayar da gudunmmawa a yakin da ake yi da 'yan ta'adda a kasashen Sahel.


A cikin gida, kasar ta Chadi na fuskantar gagarumar matsalar tsaro daga 'yan tawaye a arewacin kasar. A watan Afrilun da ya gabata Tsohon Shugaban Kasar Idriss Deby ya rasa ransa a fagen daga a yayin da ya kai ziyara ga dakarun kasar da ke yaki da 'yan tawayen da suka shigo Chadi daga kasar Libya.