China ta gudanar da gagarumin atisaye a yankin Taiwan
December 29, 2025
China ta gudanar da atisayen soji a kewayen Taiwan inda ta ce ta na killace muhimman yankuna ne na tsibirin, a matsayin gargadi ga abin da ta kira "kungiyoyin masu neman ballewa”.
Rundunar sojin kasa da ta ruwa da ta sama da kuma rundunar makamai masu linzami duk sun shiga atisayen, kamar yadda sojojin China suka bayyana.
Taiwan na bukatar zaman lafiya da China
An sanya wa atisayen suna "Justice Mission 2025”, kuma ana gudanar da shi ne kwanaki kadan bayan Amurka ta sanar da sayar wa Taiwan daya daga cikin manyan kunshin makamai mafi girma, wanda darajarsa ta kai dala biliyan 11.
Wannan mataki ya jawo zazzafar suka daga Beijing, wacce ta mayar da martani ta hanyar sanya takunkumi kan wasu kamfanonin kera makaman Amurka.
China ta kakaba wa kamfanonin Amurka 10 takunkumai
Yunkurin Taiwan na kara karfafa tsaronta a wannan shekara ya fusata Beijing, wacce ke ikirarin cewa tsibirin yankinta ne duk da cewa Taiwan na mulkin kanta.
Ofishin shugaban Taiwan ya soki atisayen sojin na China, inda ya ce hakan tamkar kalubalantar ka’idojin kasa da kasa ne.