Chavismus ohne Chavez
March 6, 2013Tsawon watanni uku kafafan yada labaru da 'yan adawa ke saka ayar tambaya ko Hugo Chavez na nan da ransa. Sai a ranar Talata da yamma Nikolas Maduro, mataimakin shugaban kasa kuma mutumin da Chavez ya nada a matsayin magajinsa ya tabbatar da mutuwar shugaban na Venezuela. Dole Nikolas Maduro ya shirya sabon zaben a cikin kwanaki 30 masu zuwa. Ba wanda ke shakka game da shirya sabon zaben, inji Leslie Wehner dan kimiyyar siyasa a cibiyar nazarin siyasa ta Jamus wato Giga dake birnin Hamburg.
"Za a gudanar da zabukan nan gaba kadan, gwamnati dake ci za ta iya yin amfani da sunan Hugo Chavez don cimma burinta. Chavez ya nada Nikolas Maduro a matsyin gajinsa, kuma ina gani hakan zai taka muhimmiyar rawa a zaben."
Tsarin jamhuriya mafi dadewa
Shi kuwa Stefan Rink na jami'ar birnin Berlin saka ayar tambaya yayi musamman game da kasashen Latunamirka.
"Ba Venezuela kadai ba, ilahirin kasashen Latunamirka kasashe ne masu dadadden tsarin jamhuriya a duniya baki daya, duk da mulki na kama karya da a rika samu. Saboda wannan dalili duk wata gwamnati ka iya tabbatar da sahihancinta ba tare da la'akari da kundin tsarin mulkin kasa ba."
Sai dai Jose Colina shugaban kungiyar 'yan kasar Venezuela da suka yi kaura kuma ke da mazauninta a birnin Miami na kasar Amirka, ya ce shin kam ba zai amince da wannan gwamnati ba.
"Ai ba wanda ya rantsar da Hugo Chavez da ilahirin majalisar ministocinsa da kuma Nicolas Maduro. Saboda haka wata haramtacciyar gwamnati ta yi amfani da haramtattun dokoki ta halasta wata gwamnati."
Magudi a zaben shekarar 2012
Tun a zaben da aka yi baya bayan nan an yi amfani da kudin kasa da kafofin yada labaru a hanyoyin da ba su dace ba, sannan a wasu wuraren an tursasa wa masu zabe. Masana na zargin cewa jam'iyar Hugo Chavez za ta yi aringizon kuri'u a zaben dake tafe, domin ci-gaba da aiwatar da akidar marigayin. Ko da yake Maduro ba ya da kwarjini kamar Chavez amma a matsayin tsohon direban bas kuma dan kwadago yana da abubuwan da zai iya yin gadara da su, kasancewa lokacin da yake rike mukamin ministan harkokin waje yayi biyayya tare da yin aiki tukuru.
Sai dai su ma 'yan adawa ka iya taka rawar gani idan suka hada kai, kamar yadda suka yi a zaben karshen shekarar 2012, inda suka tsayar da dan takara guda.
Mawallafa: Jan D. Walter / Mohammad Nasiru Awal
Edita: Mouhamadou Awal Balarabe