Ci gaba da kwato iko daga kungiyar IS
February 24, 2017![Irak Kampf um West-Mossul](https://static.dw.com/image/37701441_800.webp)
Talla
Dakarun kasar Iraki sun shiga wasu yankunan da ke yamma da birnin Mosul wani babban yanki da mayakan IS ke sheke ayarsu gabanin matsin lamba da suke fuskanta a halin yanzu. Bayanai sun ce an hango jiragen yakin kasar na lugudan wuta kan sansanonin mayakan IS a wani yanki na Syria, lamarin da wasu a Damascus suka kira hare-haren hadin guiwa ne tsakanin gwamnatocin kasashen biyu.
A wasu jerin hare-haren neman kwato birnin Mosul daga 'yan jihadin na IS, a karon farko an ga manyan jiragen yakin Irakin na ta dannawa ta gabar yammacin kogin Jordan. Bayan kwato babban filin tashi da saukar jiragen birnin na Mosul a ranar Alhamis, rahotanni sun ce ana can ana ci gaba da barin wuta musamman a wurare da ke makwabtaka da wajen da ake kira Jaw Sag.