1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ciyar da dalibai a Nijar albarkacin Azumi

04:27

This browser does not support the video element.

Gazali Abdou Tasawa M. Ahiwa
April 21, 2022

Musulmi a Nijar, sun dukufa wajen neman falalar watan Azumi wajen ciyar da dalibai a jami'a. Wannan al'ada ta ciyarwa dai na taimaka wa dalibai da dama wadanda ke madalla da samun haka.

Al’ummar Musulmin kasar Nijar na ci gaba da bin sauran takwarorinsu Musulmi na duniya wajen gudanar da Azumin watan Ramadan da ke zama daya daga cikin shika-shikan muslunci. Kuma lokacin buda baki na zama lokaci mafi mahimmanci ga mai Azumi. Sai dai al’adar buda baki na shan bam-bam daga wata kasa zuwa wata ko daga wasu iyalai zu wasu.