1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mahukuntan Chaina sun garkame wasu birane

Zulaiha Abubakar
February 1, 2020

Rahotannin da ke fitowa daga kasar Chaina sun bayyana karuwar adadin wadanda suka kamu da cutar Coronavirus da sama da mutane dubu 11,000, yayin da tuni mutane 259 suka rasa rayuka.

China: Coronavirus
Hoto: picture-alliance/AP/Chinatopix

Jami'an lafiya a Hubei yankin da yafi kowanne a kasar Chaina fuskantar cutar Corona sun bayyana cewar a yanzu akwai mutane dubu 7,153 wadanda ke fama da cutar a birnin mai dauke da al'umma kusan miliyan 11. Munin al'amarin dai ya sanya mahukuntan Chaina garkame wasu manyan biranen kasar.

Tuni Hukumar Lafiya ta duniya ta ayyana dokar ta baci kan cutar ta Corona mai saurin halaka wanda ya kamu. Kasashe da dama da suka hada da Amirka da Japan da Koriya ta Kudu da Birtaniya da kuma tarayyar Jamus sun  kwashe al'ummarsu da ke zaune a kasar ta Chaina a wani mataki na kandagarki, yayin da wasu kasashen suka zabi takaita shigar matafiya daga  Chaina. Ita kuwa kasar Rasha sanar da shirinta ta yi na rufe iyakoki tsakaninta da Chaina har sai al'amura sun daidaita.