1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Taliban ta aika jami'anta zuwa kasar Jamus

August 29, 2026

Taliban ta aike da tawagar jami'anta zuwa Jamus domin taimaka wa shirye-shiryen mayar da wasu 'yan Afghanistan zuwa kasarsu, duk da cewa Berlin ba ta amince da gwamnatin Taliban a hukumance ba.

Deutschland Berlin 2024 | Afghanische Botschaft in Berlin-Grunewald
Hoto: Friedrich Bungert/SZ Photo/picture alliance

Gwamnatin Taliban ta Afghanistan ta aike da wata tawagar jami'an diflomasiyya zuwa Jamus, kamar yadda gidan rediyon NDR na kasar ya ruwaito.

Jami'an uku za su shafe makonni uku a Jamus, kuma a halin yanzu suna ofishin jakadancin Afghanistan da ke Berlin.

Ma'aikatar Harkokin Wajen Jamus ta tabbatar da kasancewar tawagar, tana mai cewa ziyarar na da nasaba da shirye-shiryen sake mayar da wasu 'yan kasar Afghanistan daga Jamus zuwa kasarsu.

Shekaru biyar bayan Taliban ta sake karbar iko a Kabul, har yanzu Rasha ce kadai ta amince da gwamnatinta a hukumance.

Tsallake zuwa bangare na gaba Babban labarin DW

Babban labarin DW

Tsallake zuwa bangare na gaba Karin labarai daga DW