Dakarun Faransa sun kai hari a kan AQMI
October 10, 2014Talla
A cikin wata sanarwa da fadar shugaban ƙasar ta bayyana, ta ce an ƙaddamar da hare-haren ne,tare da haɗin gwiwar gwamnatin Nijar a kan jerin gwanon ƙungiyar da ke kan hanyar zuwa Mali daga Libiya.
Kuma hare-haren sun yi sanadiyyar lalata makamai da tankoki yaƙi da masu kishin addini ke ɗauke da su zuwa Mali.Sannan an kama wasu da dama daga cikinsu tare kuma da sauran manyan makamai.