1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Dakarun Isra'ila sun janye daga Jenin

July 5, 2023

Rundunar sojin Isra'ila ta janye dakarunta daga wani yanki da ke hannun 'yan tawaye a gabar yamma da kogin Jordan, inda hakan ke kawo karshen farmakinta na kwanaki a yankin.

Birnin Jenin bayan da dakarun Isra'ila suka janye
Hoto: Majdi Mohammed/AP/picture alliance

Sojojin sun yi ikirarin cewa sun yi barna sosai a kan kungiyoyin 'yan ta'adda a sansanin 'yan gudun hijira da ke birnin Jenin, a hare-hare ta sama da kuma farmakin sojoji ta kasa. Gabanin janyewar dai, Firanministan Isra'ila Benjamin Netanyahu, ya sha alwashin sake kai makanmancin wannan harin idan bukatar hakan ta taso.

Tun a farkon shekarar 2022 ne, Isra'ila ke kai jerin hare-hare yankunan Falasdinawa a wani mataki da ta ce ramuwa ce ga munanan hare-haren Falasdinawan. Rahotanni sun yi nuni da cewa, mayakan Hamas sun harba wasu rokoki zuwa Isra'ila, inda ita ma Isra'ilar ta kaddamar da wasu hare-hare ta sama a wannan Larabar.

Hukumomin kiwon lafiyan Falasdinu sun ce kimanin Falasdinawa 13 ne aka kashe tun fara farmakin, sai dai dakarun Isra'ila sun yi ikrarin halaka 'yan ta'adda ne kawai.